- Motar alfarma mallakin Gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ta kama da wuta
- Farashin motar ya kai naira miliyan Arba'in da hudu
Wata motar alfarma mallakin Gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ta kama da wuta bal bal a jihar Legas a ranar Talata 24 ga watan Oktoba, inji rahoton Daily Trust.
Majiyar diranigist.com motar mai suna G-Wagon kirar Marsandi ta kai naira miliyan 44, ta kama da wuta ne yayin da take kan hanyar zuwa filin tashi da saukan jiragen jihar Legas.
Olayinka ya isar da sakon gadiya daga gwamnan ga mutanen da suka taimaka wajen kashe wutar. Wani bincike da majiyar mu tayi ya bayyana cewa farashin wannan motar ya kai dala 122,440, kimanin N43, 941, 000.
No comments:
Post a Comment