Rahotanni sun kawo cewa yayinda ake zabe a wasu bangarori na kasar Kenya, ana zanga-zanga a wasu kamar su Kisumu sannan kuma ba’a kada kuri’a ko guda ba.
Mafi akasarin titunan dake cikin birinin a toshe suke da duwatsu da tayoyi da suke ci da wuta yayin da masu zanga-zanga ke arangama da jami'an tsaro - suna musayar duwatsu da hayaki mai sa hawaye.
Zuwa yanzu ba’a kada kuri'a ko daya ba a birnin, sannan kuma cikin jami'an hukumar zabe 400 da ake tsammani za su zo, uku ne kadai suka hallara.
Har ila yau babu ko wani akwatin zabe da aka ajiye a runfunan zabe.
Kenya: An yi dauki-ba-dadi tsakanin 'yan adawa da jami'an tsaro
Haka al’amarin yake a unguwannin marasa galihu dake Nairobi inda 'yan adawa ke da rinjaye.
Sai dai a wasu bangarori na kasar ana ci gaba da gudanar da zabe, duk da cewa da alama mutane ba su fito kamar yadda suka fito ba a zaben watan Agusta wanda kotun kolin kasar ta soke.
Ana kyautata zaton cewa za a nemi alkalai su yanke hukunci kan ko za a iya amincwa da sakamakon zaben ko kuma a'a.
'Yan sanda sun yi arangama da magoya bayan 'yan adawa inda wasu daga cikinsu suke kokarin hana mutane zuwa rumfunan zabe.
Kenya: An yi dauki-ba-dadi tsakanin 'yan adawa da jami'an tsaro (hotuna)
ReplyDeletehttps://diranigist.blogspot.co.ke/2017/10/kenya-yi-dauki-ba-dadi-tsakanin-adawa.html?m=1